Blog

  • Ababen hawa sun lalace yayin da motar CNG ta yi bindiga a Kaduna

    Ababen hawa sun lalace yayin da motar CNG ta yi bindiga a Kaduna

    [ad_1]



    Aƙalla motoci biyu ne suka lalace a tashar motar Mando da ke Jihar Kaduna, biyo bayan bindiga da wata mota mai amfani da gas ɗin CNG ta yi.

    Wani ma’aikacin tashar mai suna Abdulkadir Abdullahi, ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 4 na Asuba, lokacin da tankin motar bas ɗin ya fashe a cikin tashar.

    Ya ce lamarin ya yi sanadin lalacewar motoci guda biyu, kuma an kwashe su daga wajen domin duba irin ɓarnar da aka yi.

    A cewarsa: “Abin farin ciki, babu wanda ya rasa ransa ko ya ji rauni, domin babu fasinjoji a cikin motar a lokacin da abin ya faru. Sai dai bindigar ta tsoratar da mutanen da ke wajen.”

    Abdullahi, ya kuma ƙaryata jita-jitar cewa bam ne ya fashe, yana mai cewa matsalar gas ce kawai ta haddasa lamarin.

    Rahotanni sun nuna cewa harkoki sun koma yadda aka saba a tashar, wadda ke kusa da sansanin sojojin sama na Kaduna.

    Rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, ta tabbatar da cewa ba bam ba ne ya tashi a tashar, illa matsala da ta shafi gas na wata mota.

    A wata sanarwa da kakakin rundunar, DSP Mansir Hassan, ya fitar, ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3 na Asuba a harabar kamfanin sufuri na Silver Luxury Travel.

    Ya ce: “Ƙarar fashewar ce ta sa wasu suka ɗauka cewa bam ne. Amma bincike ya nuna cewa tankin wata mota ne ya fashe, saboda an cika shi fiye da ƙima.”

    Rundunar ta ce babu wanda ya mutu ko ya ji rauni, sannan an killace wajen domin tabbatar da tsaro.

    Kwamishinan ’yan sandan jihar, Muhammad Rabiu, ya ba da umarnin gudanar da bincike domin gano ainihin dalilin faruwar lamarin.

    Haka kuma, rundunar ta buƙaci jama’a da su guji yaɗa jita-jita, musamman kan lamuran tsaro, domin kauce wa ruɗani.


    [ad_2]

    Source link

  • Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya bayyana cewa wannan

    Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya bayyana cewa wannan

    Welcome to WordPress. This is your first post. Edit or delete it, then start writing!

  • Sojoji Sun Kwato Yankuna, Sun Kashe Ƴan Bindiga 65 A Zamfara

    Sojoji Sun Kwato Yankuna, Sun Kashe Ƴan Bindiga 65 A Zamfara

    [ad_1]

    Dakarun Operation FANSAR YAMMA sun samu gagarumar nasara a yaƙi da ‘yan bindiga a jihar Zamfara, inda suka kashe aƙalla ‘yan bindiga 65 ciki har da ɗan wani fitaccen jagoran ‘yan bindiga da ake nema ruwa a jallo, a wani zazzafan farmaki da aka kai ta ƙasa da sama a ƙaramar hukumar Tsafe.

    Rahotanni sun nuna cewa harin ya auku ne a ƙauyen Munhaye da ke bayan Kunchin Kalgo, inda aka kashe Kachalla Iliya Sarki, wanda ke daga cikin manyan kwamandojin ƙungiyar kuma ɗan Ado Allero, tare da wasu manyan jagorori irin su Dogo Sule da Iliya Mai Rasha, waɗanda ake zargi da hannu a hare-hare da garkuwa da mutane a yankin Arewa maso Yamma.

    • Motoci 3 Masu Amfani Da Gas (CNG) Sun Yi Bindiga A Tashar Mota A Kaduna
    • Gwamna Bago, Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Bindiga Da Masu Ba Su Bayanai

    Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa an fara gumurzu mai tsanani ne da misalin ƙarfe 6:00 na yammacin ranar Asabar, 4 ga Afrilu, 2026, inda ɗaruruwan ‘yan bindiga ɗauke da makamai suka kai hari da babura kusan 300 daga yankunan Yan Wari da sansanin Dankarami Gwaska, amma dakarun sojoji tare da taimakon hare-haren jiragen sama suka daƙile su bayan shafe sama da sa’o’i bakwai ana musayar wuta.

    Sai dai duk da wannan nasara, an yi asarar rayukan wasu jami’an ‘yan sa-kai guda bakwai da suka taimaka wa sojojin a fafatawar, yayin da rahotanni ke cewa Ado Allero ya tsere daga yankin zuwa garin Yankuzu, inda ake zargin yana ɓoye, yayin da sojoji ke ci gaba da farautarsa da sauran mabiyansa domin murƙushe su gaba ɗaya.

    Masana harkokin tsaro sun bayyana kashe Iliya Sarki a matsayin babbar koma baya ga ‘yan bindiga a yankin, suna mai cewa hakan zai raunana tsarin jagoranci da ayyukan ƙungiyar, sai dai sun yi gargadin cewa hakan na iya haifar da ramuwar gayya, don haka an sanya jami’an tsaro cikin shirin ko-ta-kwana a yankunan da ke cikin haɗari yayin da ake ci gaba da aikin share yankunan daga ragowar ‘yan bindigar.

    [ad_2]

    Source link

  • Shugaba Tinubu Ya Amince Da Biyan Naira Tiriliyan 3.3 Domin Warware Bashin Wutar Lantarki

    Shugaba Tinubu Ya Amince Da Biyan Naira Tiriliyan 3.3 Domin Warware Bashin Wutar Lantarki

    [ad_1]

    Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da wani shirin biyan kuɗi har Naira tiriliyan 3.3 domin warware tsofaffin basussukan da suka addabi ɓangaren wutar lantarki, a wani mataki da ake ganin zai taimaka wajen farfaɗo da tsarin samar da wuta da kuma inganta ayyukansa gaba ɗaya.

    Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya bayyana cewa wannan mataki ya biyo bayan cikakken nazari kan basussukan da suka taru tsawon sama da shekaru goma, daga watan Fabrairu na 2015 zuwa Maris 2025, inda aka tabbatar da cewa adadin Naira tiriliyan 3.3 shi ne cikakken kuɗin da za a biya domin rufe wannan lamari gaba ɗaya.

    • 2027: Gwamna Ododo Ya Shirya Gangamin Goyon Bayan Tinubu A Kogi
    • 2027: Tinubu Na Son A Naɗa Shi Sarauta Ne, Ba Zaɓe Ba — Dino Melaye

    Ya ƙara da cewa tuni aka fara aiwatar da shirin, inda tashoshin samar da wutar lantarki guda 15 suka rattaba hannu kan yarjejeniyar karɓar bashin da ya kai Naira tiriliyan 2.3, yayin da gwamnatin tarayya ta tara Naira biliyan 501 domin fara biyan kuɗin, ciki har da Naira biliyan 223 da aka riga aka fitar, tare da ci gaba da sauran biyan kuɗaɗen a matakai na gaba.

    Masu ruwa da tsaki na ganin cewa wannan mataki zai ƙarfafa dukkan sassan tsarin wutar lantarki, tare da inganta daidaiton samar da wuta da kuma rage yawan tangarɗar da ake samu, wanda hakan zai amfanar da ‘yan ƙasa da masana’antu baki ɗaya.

    Mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin makamashi, Olu Arowolo-Verheijen, ya bayyana cewa shirin ba wai biyan basussuka kawai ba ne, har ma yana da nufin dawo da amincewa a bangaren, ta hanyar tabbatar da cewa masu samar da iskar gas da tashoshin wuta suna samun haƙƙinsu, tare da inganta tsarin mitoci da farashin sabis domin ya dace da ingancin wutar da ake samu.

    A ƙarshe, Shugaba Tinubu ya yaba da gudunmawar da masu ruwa da tsaki suka bayar wajen warware wannan matsala, yana mai tabbatar da cewa mataki na gaba na shirin, wato Series II, zai fara a wannan kwata, domin ci gaba da gyaran ɓangaren wutar lantarki da bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa.

    [ad_2]

    Source link

  • Ababen hawa sun lalace yayin da motar CNG ta yi bindiga a Kaduna

    Ababen hawa sun lalace yayin da motar CNG ta yi bindiga a Kaduna

    [ad_1]



    Aƙalla motoci biyu ne suka lalace a tashar motar Mando da ke Jihar Kaduna, biyo bayan bindiga da wata mota mai amfani da gas ɗin CNG ta yi.

    Wani ma’aikacin tashar mai suna Abdulkadir Abdullahi, ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 4 na Asuba, lokacin da tankin motar bas ɗin ya fashe a cikin tashar.

    Ya ce lamarin ya yi sanadin lalacewar motoci guda biyu, kuma an kwashe su daga wajen domin duba irin ɓarnar da aka yi.

    A cewarsa: “Abin farin ciki, babu wanda ya rasa ransa ko ya ji rauni, domin babu fasinjoji a cikin motar a lokacin da abin ya faru. Sai dai bindigar ta tsoratar da mutanen da ke wajen.”

    Abdullahi, ya kuma ƙaryata jita-jitar cewa bam ne ya fashe, yana mai cewa matsalar gas ce kawai ta haddasa lamarin.

    Rahotanni sun nuna cewa harkoki sun koma yadda aka saba a tashar, wadda ke kusa da sansanin sojojin sama na Kaduna.

    Rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, ta tabbatar da cewa ba bam ba ne ya tashi a tashar, illa matsala da ta shafi gas na wata mota.

    A wata sanarwa da kakakin rundunar, DSP Mansir Hassan, ya fitar, ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3 na Asuba a harabar kamfanin sufuri na Silver Luxury Travel.

    Ya ce: “Ƙarar fashewar ce ta sa wasu suka ɗauka cewa bam ne. Amma bincike ya nuna cewa tankin wata mota ne ya fashe, saboda an cika shi fiye da ƙima.”

    Rundunar ta ce babu wanda ya mutu ko ya ji rauni, sannan an killace wajen domin tabbatar da tsaro.

    Kwamishinan ’yan sandan jihar, Muhammad Rabiu, ya ba da umarnin gudanar da bincike domin gano ainihin dalilin faruwar lamarin.

    Haka kuma, rundunar ta buƙaci jama’a da su guji yaɗa jita-jita, musamman kan lamuran tsaro, domin kauce wa ruɗani.


    [ad_2]

    Source link

  • Kano Pillars Ta Lallasa Bendel Insurance A Kano

    [ad_1]

    Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta koma matsayi na 14 biyo bayan gagarumar nasarar da ta samu akan abokiyar karawarta Bendel Insurance da ci 4 da nema a wasan Mako na 33 na gasar Firimiyar Nijeriya da suka buga a filin wasa na Sani Abacha dake birnin Kano.

    Pillars ta jefa ƙwallaye biyu kafin zuwa hutun rabin lokaci ta hannun Mustaphq Jibrin a minti na 23 da kuma Chidozie Okorie minti 10 tsakanin ƙwallo ta farko da ta biyu, bayan dawowa daga hutun rabin lokaci Sai Masu Gida suka ƙara ƙwallaye biyu ta hannun Muhammad Aminu da Bernard Ovoke.

    • Kano Pillars Ta Ƙare Zagayen Farko Na Gasar Firimiyar Nijeriya A Jan Layi
    • Kano Pillars Ta Fice Daga Jan Layi Bayan Doke El-Kanemi Warriors

    Da wannan sakamakon ne ƙungiyar wadda ta lashe kofin sau 4 a tarihi ta koma matsayi na 14 a teburin gasar da maki 42 a wasanni 33 da ta buga, wasanni 5 kacal suka rage kafin a kammala kakar wasan ta bana, Pillars na fatan cigaba da samun nasara a sauran wasanninta domin cigaba da zama a gasar a baɗi.

    [ad_2]

    Source link

  • Jami’an tsaro sun hallaka ’yan bindiga 100 a Zamfara, Gwamna Lawal ya jinjina musu

    [ad_1]



    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yaba wa jami’an tsaro bisa kashe ’yan bindiga 100 a jihar.

    Gwamnatin jihar, ta ce wannan nasara na nuna ƙwazo da jarumtakar jami’an tsaro wajen kare rayukan al’umma.

    A cewar Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Mahmud Dantawasa, wannan aiki babbar nasara ce a yaƙi da rashin tsaro da ’yan bindiga a jihar.

    “Wannan nasara na nuna jajircewar jami’an tsaro, waɗanda ke sadaukar da rayuwarsu domin kare jama’a,” in ji shi.

    Gwamnatin ta ce za ta ci gaba da bai wa jami’an tsaro dukkanin goyon bayan da suke buƙata domin samun nasara.

    Ta kuma yi alƙawarin yin aiki tare da Gwamnatin Tarayya da sauran masu ruwa da tsaki a harkar tsaro.

    Ta ƙara da cewa wannan nasara wani ɓangare ne na ƙoƙarin da ake yi na kawo ƙarshen ƙungiyoyin masu aikata laifi da wanzar da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa.

    An kuma buƙaci al’ummar Zamfara su ci gaba da bai wa jami’an tsaro haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai da kuma sanya ido a cikin al’ummominsu.

    “Gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba har sai an tabbatar da tsaro a kowane yanki na jihar,” in ji sanarwar.

    Gwamnatin ta ce tana da yaƙinin cewa bisa ƙoƙari da haɗin kai, za a dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.


    [ad_2]

    Source link

  • 2027: Gwamna Ododo Ya Shirya Gangamin Goyon Bayan Tinubu A Kogi

    [ad_1]

    Gwamnan Jihar Kogi, Alhaji Ahmed Usman Ododo, ya buƙaci al’ummar ƙaramar hukumar Kogi da su haɗa kai wajen mara wa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu baya gabanin zaɓen 2027, yana mai cewa ci gaba da goyon bayan shugaban ƙasa zai taimaka wajen ƙarfafa gyare-gyaren tattalin arziƙi da kuma tabbatar da ci gaban ƙasa na dogon lokaci.

    Ododo ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar godiya da ya kai Kotokarfe a ranar Lahadi, inda ya kuma duba ayyukan raya ƙasa da ake yi a yankin, yana mai jaddada cewa ci gaba da jagoranci iri ɗaya a matakin tarayya zai tabbatar da ɗorewar manufofin da aka fara aiwatarwa tare da samar da ƙarin alfanun dimokuraɗiyya ga al’umma.

    • 2027: ADC Na Duba Yiwuwar Fitar Da Dan Takarar Shugaban Kasa Ta Hanyar Yarjejeniya — Kakakin Jam’iyya
    • Farfadowar Halittun Ruwa A Kogin Yangtze Ta Nuna Kyakkyawan Yanayi

    Ya yabawa Shugaba Tinubu kan manufofinsa da ya ce suna da hangen nesa duk da wahalhalun da ke tattare da su, yana mai cewa matakan da ake ɗauka yanzu za su haifar da daidaiton tattalin arziƙi a nan gaba, musamman ta fuskar inganta ababen more rayuwa kamar aikin gyaran hanyar Lokoja zuwa Abuja, wanda ya ce alama ce ta ƙudirin gwamnati wajen haɗa ƙasa da inganta sufuri.

    Gwamnan ya kuma nuna godiya ga Sarkin Koto-Karfi, Ohimege Igu, Dakta Seidu Akawu Salihu da al’ummar yankin bisa goyon bayan da suke bai wa gwamnati, tare da jaddada cewa haɗin kai tsakanin jama’a da shugabanni shi ne ginshiƙin samun nasara a fannin tsaro da ci gaba mai ɗorewa a jihar.

    A ƙarshe, Ododo ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta samar da dama iri ɗaya ga duk masu neman kujeru ba tare da tilas ta wa ba, yana mai cewa ikon zaɓen shugabanni yana hannun jama’a ne kawai, tare da kira ga ‘yan siyasa da su kusanci al’umma domin samun amincewarsu, domin shugabanci na gaskiya yana ginuwa ne kan hidima da yardar jama’a.

    [ad_2]

    Source link

  • Tinubu ya amince da fitar da N3.3trn don gyara wutar lantarki

    [ad_1]



    Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya amince da fitar da zunzurutun kuɗi Naira tiriliyan 3.3, domin biyan tsofaffin basussukan da suka dabaibaye ɓangaren wutar lantarki, da nufin inganta samar da ruwa a faɗin Najeriya.

    Gwamnatin Tarayya, ta bayyana cewa waɗannan basussuka sun taru ne tsawon kusan shekaru 10.

    Ta ƙara da cewa biyan waɗannan basussuka zai bai wa kamfanonin samar da wutar lantarki damar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata, tare da tabbatar da samun wuta mai ɗorewa ga ’yan kasa.

    Ya zuwa yanzu, aƙalla kamfanonin samar da wuta guda 15 ne, suka amince da tsarin biyan kuɗaɗen, inda tuni gwamnati ta fara fitar da kason farko na kuɗaɗen ga kamfanonin.

    Dangane da wannan gagarumin mataki, Kakakin Shugaban Kasa, Bayo Onanuga, ya bayyana cewa: “Wannan Naira tiriliyan 3.3 za a biya basussukan da ake bi ne.

    “An fara tura kuɗaɗen ga kamfanonin samar da wutar, ana sa ran wuta za ta inganta ga ’yan ƙasa.”

    Gwamnatin ta ƙara da cewa wannan shiri ba wai kawai zai inganta wutar lantarki ba ne, har ma zai buɗe kofofin zuba jari daga ƙasashen waje, samar da ayyukan yi, da kuma kyautata ayyukan yau da kullum a faɗin ƙasar.

    Ita ma a nata ɓangaren, Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Makamashi, Olu Arowolo-Verheijen, ta nanata cewa manufar wannan shiri ta wuce batun biyan bashi.

    “Shiri ba yana nufin iya biyan basussuka kawai ba ne; an tsara shi ne domin gyara tsarin ɓangaren wutar lantarki gaba ɗaya, ta yadda ’yan Najeriya za su samu wuta mai inganci kuma ɗorewa.”

    A ƙarshe, gwamnatin ta tabbatar da cewa za a ci gaba da gudanar da wasu gyare-gyare, waɗanda suka haɗa da inganta tsarin samar da mitoci da kuma tabbatar da cewa gidaje da masana’antu suna samun kulawa game da sha’anin wutar lantarki.


    [ad_2]

    Source link

  • Darussa Uku Da Ya Kamata Trump Ya Dauka Daga Tarihi Kan Yakin Iran

    [ad_1]

    Tarihi na neman maimaita kansa dangane da yakin da Amurka da Isra’ila suke yi kan kasar Iran tun kimanin wata guda, inda masu fashin baki da masharhanta ke kokarin gane alkiblar yakin ta hanyar komawa baya a nazarci wasu abubuwa da suka faru a tarihi. Abubuwan kuwa sun kasance guda uku:

    Mashigar ruwa ta Suez

    Tun bayan da ‘yan kungiyar Houthi na Yemen suka kaddamar da hare-hare kan Isra’ila a ranar Juma’a – hari na farko tun bayan fara yakin Amurka da Isra’ila a kan Iran – wanda hakan ke nufin an samu karin wadanda suka shiga yakin.

    Shigar Houthi cikin yakin ya sa fargaba ga duniya cewa tattalin arzikin kasar zai sake shiga wani yanayi kasancewar kungiyar tana da karfin kai hare-hare ga jiragen ruwa a Tekun Maliya musamman mashigar ruwa ta Suez Canal.

    Duk da cewa kungiyar ba za ta iya toshe hanyar da kaso 30 na zirga-zirgar jiragen dakon mai ke bi ba, da kuma kaso 15 na sufurin kayayyaki ba amma kuma za ta iya samar da tsaiko ga samun damar shigewa ta mashigar Suez. Hakan na nufin, al’amura za su kara ta’azzara bisa la’akari da yadda Iran ta rufe mashigar Hormuz.

    Wannan ne ya sa masana suka yi duba ga tarihin abin da ya faru da mashigar ruwan ta Suez Canal shekaru 70 da suka wuce wanda yake da kwatankwacin irin na abin da ke faruwa a yau.

    Lokacin da shugaban Misra, Gamal Abdel Nasser ya mayar da mashigar ruwan ta Suez Canal mallakin kasarsa a 1956, ya karbe iko da daya daga cikin hanyoyin sufurin mai a duniya. Faransa da Birtaniya da Isra’ila sun yi yunkurin sake kwace iko da mashigar amma ba su yi nasara ba.

    Ga shugaban Amurka, Donald Trump da firai ministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, tarihi ya yi nuni da wasu abubuwa masu alaka da hakan.

    “Fiye da komai, al’amarin ya kawo karshen kasancewar Birtaniya kasar da ta fi kowacce karfi,” in ji dan jaridar BBC, Jeremy Bowen. “Ita ce take da iko da yankin Gabas ta Tsakiyar tun bayan yakin duniya na daya, kuma wannan ne mafarin kawo karshen ikon nata.”

    Irin dabarun da Iran da ‘yan kungiyar Houth ke amfani da su na takaita amfani da hanyar da tattalin arzikin duniya ke gudana sun yi tunani dangane da irin matakin da Gamael Abdel Nasser ya dauka.

    A lokacin da rundunar kasashen Faransa da Birtaniya suka isa bangaren arewacin mashigar ruwan Suez din, Nasser ya nutsar da jiragen ruwa, ya toshe mashigar ta hanyar katse Turai daga rijyoyinsu na mai da ke tekun fasha, kamar yadda Alfred McCoy wani masanin tarihi na Amurka ya sanar.

    Shugaban Amurka na lokacin, Dwight D. Eisenhower wanda ya nuna damuwa da al’amarin wanda zai kara fadada yakin cacar baka da Tarayyar Turai – ya shiga cikin batun shi ma, sannan ya tilasta wa Birtaniya da Faransa su janye.

    “Ya zuwa wannan lokacin….an sanya wa Birtaniya takunkumi a majalisar Dinkin Duniya, kudinta na gab da lalacewa, kimarta ta daula mai iko ta fara dusashewa sannan kasancewarta mai fada a ji a duniya na neman mutuwa,” in McCoy.

    Sai dai kamar yadda Bowen ya ce akwai banbancin kamanceceniya tsakanin rufe mashigar Suez da ta Hormuz a yau.

    “Ba ina kokarin alakanta karfin Amurka da na Birtaniya bayan yakin duniya na biyu ba. Sai dai abin da nake kokarin fitarwa shi ne dukkannin wasu kasashe masu karfi kan samu tagomashi kuma kan fadi. Sannan bisa la’akari da irin barazanar da Amurka ke fuskanta daga China – idan a nan gaba mutane suka fara tunanin faduwar Amurka to masu nazarin tarihi ka iya alakanta faduwar tata da yakin da ta shiga ba tare da tunanin abin da zai je ya zo ba.

    Domin fahimtar illar hakan kuwa, akwai muhimmanci idan aka kalli karin darussan da tarihi ke nunawa a shekaru 70 da suka shude.

    Matsalar mai a 1973

    Daya daga cikin misalai na fili ya faru ne shekaru 20 da suka shude bayan rikicin rufe mashigar ruwan na Suez.

    “A 1973 an yi yaki tsakanin Isra’ila da Misra da Syria wanda ake kira da yakin Yom Kippur. A lokacin Amurka ta bai wa Isra’ila makamai masu yawa,” in Bowen.

    “Bayan nan kuma kasashen Larabawa sun mayar da martani ta hanyar saka takunkumin da ya janyo farashin mai ya yi tashin gwauron zabbi sannan kuma ya janyo karancin man a yammacin Turai.”

    Ministan mai na Saudiyya na lokacin, Sheikh Ahmed Zaki Yamani ya fito fili ya yi magana a kan albarkatun kasa kamar mai a 1973, wanda hakan ya shafi kasuwar man ta duniya, Ya bayyana irin ikon da kasashen Larabawa ke da shi a kan mai da “makami na mai” wanda zai iya lalata tattalin arzikin duniya.

    Takunkumin ya kwashe watanni biyar yana aiki amma kuma masana sun ce sakamakonsa ya dade yana taɓa duniya. Misali tashin farashi a Amurka da kasashen da ke dogaro ga mai a masana’antunsu – sannan kuma babban bankin Amurkar ya gaza shawo kan matsalar tsadar rayuwa.

    Duk da cewa a yanzu haka dai za a iya cewa dogaro ga mai ba kamar na shekaru 50 da suka gabata ba ne kasancewar kasashe sun fadada hanyoyin samun makamashi, to amma faruwar al’amarin ka iya zama izina ga shugaban Amurka, Donald Trump.

    Kusa da Iran da Iraki

    Masana tarihi sun ce yakin Iran da Irai da ya mamaye shekarun 1980 ka iya zama darasi na kusa-kusa ta yadda za a fahimci yadda abokan Amurka ka iya kawo cikas ga tattalin arzikin duniya.

    A lokacin yakin, Iran da Iraki duk sun yi kokarin rufe mashigar Hormuz a kokarinsu na jan hankalin manyan kasashen duniya ga rikicin.

    Ya zuwa tsakiya zuwa karshen shekarun 1980, hare-hare sun yi kamari da ta sanya Kuwait ta nemi daukin kasashen duniya domin bai wa jiragenta damar wucewa ta mashigar ruwan. Amurka ta amince domin gudun ka da Rasha wadda babbar abokiyar gabarta ce a lokacin yakin cacar baka, ta mamaye ta.

    An fara yi wa jiragen dakon mai rakiya a mashigar a wani shirin da ake kira da Operation Earnest Will, inda aka fara yi musu rakiyar a Yulin 1987 amma kuma hakan ya zamo wani abin kunya ga Amurka wanda ake yi wa kallon mai shiga tsakani – inda Iran ta kai hare-hare ga jiragen ruwan da ya kamata ta kare, a kan hanyarsu ta zuwa Kuwait.

    Masana sun ce al’amarin ya yi nuni da irin karancin karfin Amurka wajen share nakiyoyin ruwa da Iran ta shimfida a mashigar ta Hormuz wani abu da ya ci gaba da sanya tsoro a zukatan masu jirage.

    Tarihi ya fitar da darussan ga wadanda suke cikin yakin da ke faruwa a gabas ta Tsakiya kuma irin yadda suka tsaya suka fahimci darussan shi ne zai nuna irin alkibla da kuma lokacin da duniya za ta dauka wajen fuskantar wahalhalu.

    [ad_2]

    Source link